Monday, April 6, 2026
HomeKetareSojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar da tsohon shugaban ƙasar, Umaro Sissoco Embalo, a ƙarshen 2025.

Kafar yada labarai ta Al Jazeera ta rawaito cewa shugaban mulkin sojin ƙasar, Manjo-Janar Horta Inta-a, ya sanar da hakan ne a wata doka da aka sanar a ranar Laraba, inda ya ce an cika dukkan sharuddan gudanar da zaɓen cikin ‘yanci, adalci da gaskiya.

Rahoton ya bayyana cewa juyin mulkin da ya faru a watan Nuwamba ya kawar da Embalo, tare da naɗa Horta Inta-a don jagorantar gwamnatin na tsawon shekara guda.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata