Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSojojin Najeriya sun yi ajalin na hannun damar Bello Turji a Sokoto

Sojojin Najeriya sun yi ajalin na hannun damar Bello Turji a Sokoto

Sojojin rundunar 8 Division na Najeriya sun tabbatar da shafe fitaccen shugaban ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, daga duniya, a ƙaramar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto.

Majiyar tsaro da ta nemi a boye sunanta ta shaida wa manema labarai cewa an yi nasarar ajalin Kallamu ne a wani gagarumin samame da aka yi tare da haɗin gwiwar ’yan sa-kai.

Rahotan jaridar The Nation ya nuna cewa Kallamu na daga cikin manyan amintattun Bello Turji, kuma yana taka muhimmiyar rawa a ayyukan ta’addanci a yankin kafin a kawo karshen sa a wannan rangadi na musamman.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata