Monday, April 6, 2026
HomeKetareSojojin Nijeriya da ke Burkina Faso sun koka kan tsawaita zamansu a...

Sojojin Nijeriya da ke Burkina Faso sun koka kan tsawaita zamansu a kasar

Jami’an Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya (NAF) guda 11 da ke tsare a Burkina Faso sun koka kan tsawaita zamansu a kasar, suna mai kira ga gwamnatin Nijeriya musamman Ma’aikatar Harkokin Waje da ta dauki lamarin da muhimmanci.

Jami’an sun bayyana cewa suna kan tafiya ne zuwa Portugal domin gyaran jirgi, amma suka sauka a Bobo-Dioulasso sakamakon cikas din Na’ura da jirgin ya samu.

Rundunar ta NAF ta musanta zargin leken asiri ko ayyukan sirri, tana mai cewa saukar jirgin ta kasance bisa ka’idojin tsaro na jiragen saman kasa da kasa.

Daily Trust ta ruwaito mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Ebienfa, ya ce jami’an har yanzu na tsare, amma an fara tattaunawa ta diflomasiyya.

Ya bayyana cewa mukaddashin jakadan Nijeriya ya je Burkina Faso amma aka hana shi ganinsu, yayin da ake ci gaba da ganawa domin a sako su kafin Kirsimeti.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata