Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiSojojin Nijeriya sun dakile wani kwanton-bauna da Lakurawa suka yi musu a...

Sojojin Nijeriya sun dakile wani kwanton-bauna da Lakurawa suka yi musu a jihar Kebbi

Ayarin motocin Babban Kwamandan Runduna ta 8, Manjo Janar Bemgha Koughna, ya tsallake rijiya da baya bayan da dakarun sojin Nijeriya suka dakile wani hari na kwanton-bauna da ake zargin ‘yan ta’addar Lakurawa sun shirya a kusa da Tsaunin Mayama, Jihar Kebbi. Lamarin ya faru ne yayin da kwamandan ke hanyarsa ta zuwa duba dakarun da ke aiki a yankin.

Sanarwar da Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulda da Jama’a na Runduna ta 8, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya fitar ta ce dakarun sun mayar da martani cikin gaggawa bayan harin, inda suka kashe ‘yan ta’adda biyar tare da tarwatsa sauran. Ya bayyana cewa matakin ya hana maharan cimma manufarsu tare da tabbatar da tsaron ayarin.

Bayan kammala artabun, sojojin sun yi bincike a yankin inda suka kwato makamai da kayayyaki, ciki har da bindigogi, harsasai, babura biyar da kuma kudade. Rundunar ta ce dakarunta na ci gaba da sintiri domin hana sake faruwar hare-hare, tare da jaddada kudurin sojin Nijeriya na kare fararen hula da murkushe barazanar ‘yan ta’adda.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata