Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraisojojin Nijeriya sun yi ajalin ‘yan bindiga uku a jihar Kogi

sojojin Nijeriya sun yi ajalin ‘yan bindiga uku a jihar Kogi

Dakarun 12 Brigade na Sojojin Nijeriya sun yi nasarar kawo karshen ‘yan bindiga uku tare da kama wanda ake zargin mai samar musu da kayayyaki a yayin wani samame a Kabba Bunu da Yagba West a Jihar Kogi.

Aikin ya gudana ne a ranar Asabar 3 ga Janairu, 2026, bayan samun bayanan sirri kan motsin ‘yan bindiga.

Jaridar Punch ta ruwaito Lt. Hassan Abdullahi, na cewa sojojin sun yi musu kwanton-bauna inda aka yi artabu da bayarayin, lamarin da ya tilasta ‘yan bindigar janyewa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata