Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiTinubu na shirin fitar da sunayen sabbin Jakadun Nijeriya

Tinubu na shirin fitar da sunayen sabbin Jakadun Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu na shirin fitar da jerin sunayen jakadu da za su wakilci Nijeriya a manyan kasashe cikin makonni masu zuwa, a cewar majiyoyi daga fadar shugaban kasa.

Wannan mataki na zuwa ne bayan damuwar da jama’a ke nunawa kan yadda rashin jakadu ya rage karfin diflomasiyyar Nijeriya, musamman a kasashen da ke da muhimmanci ga hulɗar ƙasa da ƙasa.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Tinubu ya janye dukkan tsoffin jakadu a watan Satumban 2023 domin sake fasalin manufofin ƙasar a ketare, sai dai jinkirin tantance sababbin jakadu ya kai shekara biyu ba tare da sabbin nade-naden ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata