Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaTinubu ne ke da rijayen kuri'un Rivers a zaben 2027 - Gwamna...

Tinubu ne ke da rijayen kuri’un Rivers a zaben 2027 – Gwamna Fubara

Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya bayyana cewa zai jagoranci kokarin tabbatar da nasarar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027, yana mai cewa hadin kai tsakanin jihar da gwamnatin tarayya zai kara wa Rivers ci-gaba.

Fubara, wanda ya yi wannan jawabi yayin kaddamar da hanyar Egbeda–Omerelu mai tsawon 12km, ya ce zai yi duk abin da ya dace domin tabbatar da zaman lafiya a jihar, saboda ci-gaba ba ya zuwa idan rikici ya yi yawa.

Ya jaddada cewa gwamnatin sa za ta yi aiki tare da dukkan kungiyoyin goyon bayan Tinubu domin ganin an samu nasara a 2027.

A gefe guda, wata kungiya a APC ta kare ficewar Fubara daga PDP, tana cewa matakin ba kuskure ba ne, illa martani ga rikice-rikicen cikin gida da suka addabi PDP.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata