Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiTinubu ya kare Nijeriya daga faɗawa rikicin farashin mai da kasashen Duniya...

Tinubu ya kare Nijeriya daga faɗawa rikicin farashin mai da kasashen Duniya ke fama da shi – Uzodimma

Gwamnan jihar Imo State, Hope Uzodimma, ya ce shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya kare ƙasar daga mummunan rikicin farashin mai da ya addabi kasashen duniya sakamakon rikicin Gabas ta Tsakiya, duk da cewa farashin litar mai ya kai kusan N1,300 a Nijeriya.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Uzodimma ya bayyana hakan ne lokacin da ya karɓi baƙuncin wata tawaga ta kungiyar City Boy Movement a gidan gwamnati da ke Owerri a karshen mako.

Gwamnan ya ce rikicin da ya ɓarke tsakanin Iran, Israel da kuma Amurka ya haifar da tashin farashin mai a duniya, musamman bayan da aka samu matsala a mashigar jiragen ruwa ta Strait of Hormuz, wadda kusan kashi 20 cikin 100 na man fetur na duniya ke bi ta cikinta.

Duk da haka, Uzodimma ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu ta aiwatar sun taimaka wajen kauce wa karancin mai da kuma hauhawar farashi fiye da haka a cikin gida.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata