Monday, April 6, 2026
HomeKetareTrump zai haramta wa 'yan Nijeriya komawa Amurka da zama

Trump zai haramta wa ‘yan Nijeriya komawa Amurka da zama

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana sabon tsari da yake neman dakatar da shigar mutane Amurka daga kasashe daban-daban ciki har da Nijeriya.

Trump ya sanar da hakan ne yayin yayin wani biki inda ya ce tsarin da ake amfani da shi yanzu ya janyo tabarbarewar tsaro da matsin lamba ga hidimomin gwamnati.

Jaridar Daily Trust, ta rawaito Trump na cewa, yawan ’yan kasashen waje da ke zaune a Amurka ya kai mutum miliyan 53, abin da ya ce ya taimaka wajen yawaitar laifuka, cunkoso a asibitoci da kuma tashe-tashen hankula.

Shugaban ya yi zargin cewa shigowar ’yan gudun hijira daga Somalia zuwa Minnesota, ya sauya yanayin al’ummar jihar ta hanyar da ya ce ba ta da kyau.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata