Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiTsadar bukukuwa da shirye-shirye na hana matasa yin aure - Gwamnatin Sokoto

Tsadar bukukuwa da shirye-shirye na hana matasa yin aure – Gwamnatin Sokoto

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayyana cewa tsadar shirye-shirye na hana matasa da dama yin aure, lamarin da ya sa gwamnati ke shirin tabbatar da bin dokar da ke hana yin almubazzaranci wajen shirye-shiryen sa.

 

Gwamna Ahmed Aliyu ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da Daraktan yaɗa labarai na fadar gwamnati Abubakar Bawa ya fitar.

 

A cewar sanarwar, gwamnan ya nuna damuwa kan yadda nauyin kuɗaɗen da ake ɗora wa ma’aurata kafin aure ke ƙara wahalar da samun aure.

 

Gwamnan ya ce wannan dabi’a ta sa yawan mutanen da ba su yi aure ba ya ƙaru a jihar, wanda hakan ke haifar da yawaitar rashin tarbiyya a tsakanin matasa da ba su da hali su biya kuɗaɗen da ake buƙata kafin auren.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata