Ministan yaɗa labarai da wayar da Kan jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ya ce manufofin Shugaba Bola Tinubu na fara magance matsalar ficewar ƙwararrun likitoci (japa) da sauran ƙalubalen lafiya a Nijeriya.
Idris ya bayyana hakan ne a Abuja yayin bikin rantsar da daliban MBBS na jami’ar Nile ajin 2025, inda ya ce sabbin likitocin za su taimaka wajen inganta harkar kiwon lafiya da gwamnatin tarayya ke kokarin gyarawa.
A cewarsa, gwamnati na ƙirƙirar yanayi mai kyau da zai sa ƙwararru su zauna su yi aiki a gida, yana mai ƙara da cewa tuni wasu da suka bar ƙasar suna komowa Nijeriya, sakamakon sabbin tsare-tsaren da aka kafa, musamman a bangaren lafiya.
