Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiTsare-tsaren Tinubu ya sanya Nijeriya kan gaba wajen samun masu zuba jarin...

Tsare-tsaren Tinubu ya sanya Nijeriya kan gaba wajen samun masu zuba jarin makamashi a Afrika – Hadimin Shugaban Nijeriya

Nijeriya ta sake zama babbar cibiyar jawo jarin makamashi a yankin Afirka ta Kudu da Sahara, bayan ta karɓi kashi 38 cikin 100 na manyan ayyukan makamashi da aka amince da su a nahiyar cikin watanni 24 da suka gabata.

Mai bai wa Shugaban Nijeriya shawara kan harkokin makamashi, Olu Verheijen, ta ce ƙasar ta jawo jarin dala biliyan 5.3 a bangaren hako mai da gas a shekarar 2025 kaɗai.

Verheijen ta bayyana cewa wannan ci gaba ya zo ne duk da raguwar kashe kuɗi da kashi 18 cikin 100 a yankin, lamarin da ke nuna cewa Nijeriya ta rabu da koma bayan yankin baki ɗaya. Ta ce gyare-gyaren da aka yi sun dawo da amincewar masu zuba jari, inda Nijeriya ta samu manyan ayyuka 5 daga cikin 8 da aka amince da su a Afirka cikin shekaru biyu kacal.

Ta kara da cewa aikin Shell–Sunlink HI Field (OML 144) da aka amince da shi a 2025, tare da sabbin tsare-tsaren ƙarfafa hako gas da aka ƙaddamar a 2024, sun taka muhimmiyar rawa wajen wannan nasara.

Verheijen ta ce ana sa ran wannan gagarumin ci-gaba zai ci gaba zuwa 2026, tare da bukatar hukumomi su sauya tsofaffin tunani domin sauƙaƙa zuba jari da bunƙasa ƙwarewar ’yan Nijeriya a bangaren makamashi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata