Ministan sufurin jiragen sama na Nijeriya Festus Keyamo, ya gargadi jam’iyyar PDP cewa tana iya fuskantar babban koma baya a shirin ta na tunkarar 2027, idan har ta tsayar da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ko kuma tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, a matsayin ɗan takara.
A wani dogon rubutu da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Lahadi, Keyamo ya ce jam’iyyar adawar tana cikin “hali mai rauni” tun bayan da ta kasa tsayar da tikitin shugabancin ta na 2023 ga yankin Kudu — abin da ya ce ya sa PDP ta rasa goyon baya a wuraren da take da karfi a baya kamar Kudu maso Kudu da Kudu maso Gabas.
Keyamo ya bayyana cewa tsayar da Jonathan ɗan takara na iya haifar da cikas na doka bisa sashen 137(3) na Kundin Tsarin Mulkin 1999 (wanda aka yi wa gyara), wanda ya nuna cewa duk wanda aka rantsar sau biyu a matsayin shugaban ƙasa ba zai sake tsayawa takara ba.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar za ta ɗauki alhakin kawar da ido kan wannan batun idan ta tsayar da shi sannan daga bisani aka soke takararsa bayan an rufe tsayar da ɗan takara.
Tsayar da Good Luck Jonathan ko Peter Obi a matsayin ɗan takarar shugaban kasa ba alheri ne ga PDP ba – in ji wani ministan Tinubu
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
