Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiTsoffin sojoji sun mamaye hedikwatar ma’aikatar kuɗi a Abuja

Tsoffin sojoji sun mamaye hedikwatar ma’aikatar kuɗi a Abuja

Wasu tsoffin sojojin Nijeriya da suka ajiye aikin soja da yardarsu sun gudanar da zanga-zanga a gaban hedikwatar ma’aikatar kuɗi ta kasa a Abuja a ranar Litinin, inda suka rufe babbar ƙofar shiga ginin.

Zanga-zangar, wadda ta fara misalin ƙarfe 10:15 na safe, ta samu halartar jami’an tsaro da dama daga ɓangarorin sojoji, ‘yan sanda da kuma Hukumar DSS, domin hana barkewar rikici da kare dukiyoyin gwamnati.

Yayin da yake magana da Daily Trust, ɗaya daga cikin jagororin masu zanga-zangar, Staff Sergeant Simon Ipwu, ya bayyana cewa rashin biyan su kuɗaɗen alawus na ajiye aiki da inshora ne manyan dalilan da suka tilasta musu fita zanga-zanga.

Ya ce sun gaji da alkawuran gwamnati, kuma suna buƙatar a biya su hakkokinsu domin su rayu cikin mutunci.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata