Jagororin jam’iyyar PDP na yankin Arewacin Nijeriya sun amince da tsohon Ministan Harkoki. A Musamman, Tanimu Turaki (SAN), a matsayin ɗan takarar da suka amince domin ya yi takarar kujerar shugabancin jam’iyyar PDP na ƙasa, gabanin babban taron jam’iyyar da za a gudanar a watan Nuwamba a Ibadan, Jihar Oyo.
Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, shi ne ya sanar da hakan bayan taron shugabannin PDP na Arewa da aka gudanar a Abuja daren Laraba, inda ya bayyana cewa Turaki ne ɗan takarar da aka cimma matsaya a kansa.
Ya kuma ce duk wanda bai gamsu da wannan matsaya ba, yana da ‘yancin tsayawa takara.
Jaridar Punch ta ruwaito a baya cewa tsohon gwamnan Kaduna, Ahmed Makarfi, tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido da kuma Tanimu Turaki, sune kan gaba wajen neman wannan kujera, wacce za a yanke hukunci kanta a taron masu ruwa da tsaki na yankin a wannan makon.
Tsohon Minista Tanimu Turaki ya zama ɗan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na Arewa
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
