Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiWaɗanda suka kitsa rikicin gida a PDP ne ke ta ficewa, in...

Waɗanda suka kitsa rikicin gida a PDP ne ke ta ficewa, in ji Bode George

Jigo a jam’iyyar PDP, Cif Bode George, ya bayyana cewa mutanen da suka haifar da rikicin cikin gida a jam’iyyar su ne ke barin jam’iyyar yanzu, yana mai nuni da ficewar tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a 2023, Atiku Abubakar, da Dele Momodu, wanda shima ya fice daga jam’iyyar a ranar Alhamis.

Cif Bode George ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na Channels TV a ranar Alhamis.

Yayin da yake mayar da martani kan ko PDP za ta iya tsayawa da ƙafafunta bayan ficewar fitattun mutane kamar Atiku da Dele Momodu.

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP za ta koma kan turbar da ta dace bayan taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) da aka shirya gudanarwa mako mai zuwa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata