Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiWadanda suka soke ni a baya yanzu yabo na suke - Olusegun...

Wadanda suka soke ni a baya yanzu yabo na suke – Olusegun Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo, ya ce ba za a taɓa gujewa suka ba a mulki, amma wadanda ke suka a yau su ne ke zama masu yabo a gobe.

Obasanjo ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Ibadan yayin da yake ƙaddamar da tashar mota ta zamani a Iwo Road, Ibadan, wanda Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya gina domin sauƙaƙa zirga-zirga a birnin.

Tsohon shugaban ƙasar ya ce Makinde ya cancanci yabo saboda ayyukan raya ƙasa da ke sauƙaƙa rayuwar jama’a.

Ya ce shima haka aka yi da shi lokacin yana shugaba amma yanzu masu sukar sa su ne ke yi masa godiya da kuma yaba masa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata