Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiWani yaro dan shekaru 16 ya halbe abokinsa da bindiga yayin da...

Wani yaro dan shekaru 16 ya halbe abokinsa da bindiga yayin da suke wasa a jihar Niger

Wani yaro mai shekaru 16 mai suna Emmanuel Danladi ya harbe abokinsa Titus Joseph mai shekara 15 har lahira da bindigar mahaifinsa a garin Kwamba da ke Suleja a Jihar Niger.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da yaran biyu ke wasa a gidan Emmanuel, inda ya dauki bindigar da mahaifinsa Danladi Baba ke amfani da ita a kungiyar sa-kai, ya harbi abokin nasa a ciki, wanda daga bisani ya mutu.

Mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar, Wasiu Abiodun, ya ce an kama Emmanuel da mahaifinsa, sannan aka kai gawar mamacin babban asibitin Suleja yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata