Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiWata dattijuwa ta barke da kuka bayan an hanata kada kuri'a

Wata dattijuwa ta barke da kuka bayan an hanata kada kuri’a

Wata datijuwa mai shekaru 96 a duniya, Mrs. Elizabeth Onike, ta barke da kuka a rumfar zaɓe saboda an hana ta kada kuri’a a Anambara

Dattijuwar wadda ke zabe a akwatin Umudim Akasi Polling Unit 019, Agulu II, Ward 8, a ƙaramar hukumar Anaocha, jihar Anambra, a ranar Asabar.

Da take magana cikin harshen Igbo, tsohuwar ta bayyana takaicinta cewa a nan take yin zaɓe tun da dadewa.

Rahoton jaridar Punch ya ce ta ma kada kuri’a a zaɓen da ya gabata, amma yanzu jami’an INEC suna cewa katinta ba shi da inganci.

Elizabeth ta ji takaici matuka saboda ba za ta kada kuri’a a wannan zaɓen ba, wanda zai tantance wanda zai zama sabon gwamna ta.

Lamarin ya jawo tausayawa da damuwa daga wasu masu zaɓe da ke wajen, inda da dama suka yi kira ga hukumar INEC da ta duba irin waɗannan matsaloli domin kare haƙƙin zaɓen tsofaffi a nan gaba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata