Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiWike na rikewa Tinubu duk filin da gwamnati ta kwace a Abuja...

Wike na rikewa Tinubu duk filin da gwamnati ta kwace a Abuja – Hadiminsa

Hadimi ga ministan Abuja Nyesom Wike, Lere Olayinka ya bayyana cewa duk wani fili da gwamnati ta kwace iko da mallakarsa a birnin na kasancewa a hannun ministan ne cikin aminci don ya rikewa shugaban Nijeriya Bola Tinubu.

Olayinka ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na Arise, yana mai cewa a halin yanzu akwai filaye akalla 1000 da aka kwace ikon mallakar tasu, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Ya bayyana cewa kwacewar na zuwa ne sakamakon rashin bin ka’idoji ko kuma biyan wasu hakkoki daga mamallakansu.

Ya kara da jaddada cewa duk wanda ya karya doka, tabbas za ta yi aiki a kansa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata