Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiWike ya musanta zargin cewa yana goyon bayan Tinubu a boye

Wike ya musanta zargin cewa yana goyon bayan Tinubu a boye

Ministan Abuja Nyesom Wike ya musanta zargin da wasu ke yi cewa yana goyon bayan Tinubu a ɓoye, yana mai jaddada cewa matsayarsa ta siyasa a fili take kuma ba ta taɓa canzawa ba.

Wike ya yi wannan bayani ne yayin da ya ke mayar da martani kan wasu kalamai da aka danganta da gwamnan jihar Rivers Siminalaye Fubara, wanda ya bayyana cewa wasu ’yan siyasa na yin yarjejeniya a boye.

A farkon watan Disamba gwamna Fubara ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, bayan wata ganawa ta sirri da Shugaba Tinubu a Abuja, matakin da wasu ke ganin wata dabara ce ta siyasa gabanin babban zaɓe mai zuwa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata