Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaWike ya nemi hadin kan 'yan siyasa a Rivers da su dunkule...

Wike ya nemi hadin kan ‘yan siyasa a Rivers da su dunkule wuri guda su mara wa Tinubu baya a 2027

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’ummomi a jihar Rivers da su ƙara haɗin kai da fahimtar juna domin tabbatar da samun cin ribar dimokuraɗiyya.

Wike ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a, yayin ziyara a karamar hukumar Andoni, wadda ta zama wuri na 20 inda yake ziyartarsu domin gode wa al’ummar kan goyon bayan da suka bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a zaɓen 2023 tare da neman karin goyon baya a gabanin zaɓen 2027.

Tsohon Gwamnan Rivers ya ce manyan jam’iyyun siyasa a jihar sun haɗu ƙarƙashin inuwa guda inda ya bukaci shugabannin al’umma su ci gaba da aiki tare domin Tinubu ya dawo a karo na 2 a zabe mai zuwa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata