Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da harin da aka kai wa Cocin Cherubim and Seraphim a garin Ejiba, karamar hukumar Yagba ya Yamma, da safiyar Lahadi, wanda ya jefa al’umma cikin tashin hankali.
Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ne ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar daga Lokoja, yana kuma Allah-wadaran harin da ’yan bindiga suka kai wa coci tare da sace fasto, matarsa da wasu masu ibada.
A cewar rahoton jaridar Punch, harin ya tayar da hankalin jama’a, inda mazauna yankin suka tsere domin neman tsira, yayin da gwamnati ke tabbatar da cewa tana ƙoƙarin kubutar da dukkan mutanen da aka sace.
