Monday, April 6, 2026
HomeLabarai'Yan bindiga sun kai hari a wani kauye na jihar Kebbi

‘Yan bindiga sun kai hari a wani kauye na jihar Kebbi

’Yan bindiga sun kai hari a kauyen Gebbe da ke karamar hukumar Shanga a jihar Kebbi, inda rahotanni ke nuna an rasa rayuka yayin da wasu da dama suka jikkata.

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa al’ummar yankin sun ce harin ya faru ba zato ba tsammani, lokacin da ’yan bindigar suka shigo kauyen suka fara harbe-harbe babu kakkautawa, lamarin da ya tilasta mazauna wurin tserewa zuwa dazuzzuka domin tsira.

Rahotanni sun ce cewa har zuwa wannan lokaci ba a tantance adadin waɗanda suka mutu ko suka jikkata ba, saboda girman harin da kuma yadda jama’a suka watse zuwa wurare daban-daban bayan harin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata