Monday, April 6, 2026
HomeLabarai'Yan bindiga sun kakaba wa manoma harajin dubu 50 ga kowace gona...

‘Yan bindiga sun kakaba wa manoma harajin dubu 50 ga kowace gona a jihohin Kano da Katsina kafin su girbe gonarsu

’Yan bindiga da ke tsakanin jihohin Kano da Katsina sun kakaba haraji ga manoma har ₦50,000 a kowace eka ga manoma, musamman masu noman rake, kafin su girbe amfanin gonarsu.

Jaridar The Guardian ta bayyana cewa ’yan bindigar sun kafa sansanoni a Dajin Rugu da ke karamar hukumar Faskari a jihar Katsina da kuma Dajin Falgore a karamar hukumar Doguwa a jihar Kano, inda suke karɓar haraji da yi wa manoman barazana.

Rahoton ya nuna cewa manoman da suka ƙi biyan harajin na fuskantar barazana, lalata amfanin gona, da yiwuwar kai musu hari, lamarin da ya tilasta wa da dama barin gonakinsu,kuma yawanci manoman rake ne suka fi fuskantar wannan matsala.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata