Yan bindiga dauke da makamai sun kwashe shanu sama da 500 a Kasuwar Daji, Karamar Hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara.
Shugaban MACBAN a jihar, Aminu Garba, ya ce harin ya faru da daddare, inda ’yan bindigar da suka haura 50 suka tsere ta bangaren daji. Ya ce an samu dawo da kusan shanu 60 daga cikin wadanda suka watse.
Wani wanda abin ya shafa, Alhaji Sani Yaba Ajiyan Fawa, ya koka kan rashin daukin gaggawa duk da kusancin jami’an tsaro, yayin da MACBAN ke cewa ana daukar matakai domin gano sauran shanun.
