Monday, April 6, 2026
HomeLabarai'Yan bindiga sun sake yin barna a jihar Katsina

‘Yan bindiga sun sake yin barna a jihar Katsina

Aƙalla mutane uku ne ake fargabar sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon wani hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Jikamshi da ke ƙaramar hukumar Musawa a jihar Katsina.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:10 na yammacin ranar Talata, lokacin da wasu mazauna garin ke shirin buɗe baki a rana ta 21 ga watan Ramadan, inda ‘yan bindigar suka riƙa harbi ba kakkautawa tare da jefa al’umma cikin firgici.

Rahotanni sun ce maharan sun kuma shiga shaguna daban-daban a garin, inda suka wawushe kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Mutanen da suka jikkata a harin an garzaya da su asibiti domin samun kulawar likitoci.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata