Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai‘Yan bindiga sun yi ajalin wani magidanci tare da garkuwa da iyalinsa...

‘Yan bindiga sun yi ajalin wani magidanci tare da garkuwa da iyalinsa a jihar Kebbi

Wasu ‘yan bindiga sun yi ajalin wani mutum mai suna Sufiyanu Garba mai shekaru 35 tare da yin garkuwa da mai dakinsa a unguwar Badariya da ke Birnin Kebbi a Jihar Kebbi.

Mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar, Bashir Usman, ya ce an kai mamacin asibitin Sir Yahaya Memorial inda likita ya tabbatar da rasuwarsa, yayin da aka ajiye gawarsa a dakin ajiye gawa.

Ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar ya umarci sashen binciken manyan laifuka su karbi shari’ar domin bincike tare da kokarin ceto matar da aka sace da kuma kamo wadanda suka aikata laifin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata