Monday, April 6, 2026
HomeLabarai'Yan bindiga sun yi garkuwa da manoma 20 a jihar Neja

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da manoma 20 a jihar Neja

Akalla mutane 20 ne wadanda suka kunshi manoma, mata masu juna biyu da kuma yara ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a kauyen Unguwan Kawo da ke yankin Erena da ke karamar hukumar Shiroro a jihar Neja.

Mazauna yankin sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 na yammacin Laraba, 26 ga Nuwamba, a lokacin da manoman ke girbin shinkafa.

A cewar wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa yace dansa na ɗaya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su, inda ya ce gonar da abin ya faru tana da tazarar kimanin mita 500 ne kacal da Erena, inda sansanin sojoji yake.

Lamarin ya faru ne kwanaki shida bayan sace dalibai da malamai sama da 200 daga makarantar St. Mary a Papiri, Karamar Hukumar Agwara.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, SP Wasiu Abiodun, ya ce zai bincika tare da tabbatar da sahihan bayanai nan gaba kadan.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata