Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai‘Yan Ibo ne ke da alhakin tashin hankali a Kudu Maso Gabas,...

‘Yan Ibo ne ke da alhakin tashin hankali a Kudu Maso Gabas, ba Fulani makiyaya ba – Gwamna Soludo

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya bayyana cewa mafi yawan garkuwa da mutane da kashe-kashe da ake yi a jihar Anambra da sauran jihohin Kudu maso Gabas ‘yan Ibo ne ke aikata su, ba Fulani makiyaya ba kamar yadda ake yawan zargi.

Soludo ya bayyana hakan ne a wajen wani taron tattaunawa da ‘yan asalin Anambra da ke zaune a ƙasashen waje, wanda aka gudanar a jihar Maryland, da ke Amurka.

Ya ce kashi 99.99 cikin 100 na masu garkuwa da mutane da sauran masu laifi da aka kama tun lokacin da ya hau kujerar gwamna shekaru uku da suka wuce, duk ‘yan Ibo ne.

A cikin wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, an ji Soludo na cewa ba Fulani makiyaya ba ne ke addabar Kudu maso Gabas, sai dai ‘yan asalin yankin da suka fake a dazuka suna aikata laifuka domin samun kudi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata