Kungiyoyin farar hula da jam’iyyun adawa a jihar Kebbi sun nuna rashin jin daɗinsu kan matakin da ‘yan majalisar dokokin jihar na ba da gudummawar motoci guda 25 ga ƙungiyar siyasa mai suna Tinubu/Kaura 2 Terms (TKT), wadda ke fafutukar ganin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Nasir Idris sun samu wa’adin mulki na biyu a 2027.
Rahotanni sun bayyana cewa motocin da aka bayar kowacce daga cikinsu na tsakanin naira miliyan 3.5 zuwa miliyan 6, bisa farashin motoci a shafin Cars45.com.
Shugaban majalisar dokokin Kebbi, Alhaji Muhammad Usman-Zuru, ne ya miƙa motocin ga ƙungiyar a madadin sauran mambobin majalisar guda 25, yana mai cewa hakan na cikin alkawarin da suka dauka lokacin da aka ƙaddamar da ƙungiyar a ranar 20 ga Mayu, 2025.
Sai dai wannan mataki ya haifar da ce-ce-ku-ce daga ‘yan adawa da masu fafutuka, inda suka zargi majalisar da cin amanar jama’a da amfani da dukiyar gwamnati don biyan bukatun siyasa.
Masu suka sun bayyana cewa bai kamata ‘yan majalisar da ke matsayin wakilan jama’a ta maida kanta ‘yan kamfen ba, musamman a lokacin da ake fuskantar matsaloli na tattalin arziki da bukatar kashe kudi a bangarori masu mahimmanci kamar lafiya, ilimi da ababen more rayuwa.
‘Yan majalisar dokokin jihar Kebbi sun ba da gudunmuwar motoci 25 don yakin neman zaben Shugaba Tinubu a 2027
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
