Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai‘Yan sanda sun hallaka ‘yan bindiga 3 tare da ceto wasu a...

‘Yan sanda sun hallaka ‘yan bindiga 3 tare da ceto wasu a wasu kauyukan iyakokin jihar Gombe

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta tabbatar da hallaka wasu ‘yan bindiga uku tare da kwato makamai da harsasai, sannan ta ceto wasu daga cikin mutanen da aka sace a wani samame da aka gudanar a yankunan kan iyakar jihar.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce jami’an tsaro sun dakile yunkurin hari a yankunan Pindiga, Billiri da Shongom ranar Juma’a, amma ‘yan bindigar sun kai hari Garin Galadima da ke yankin Lambo da misalin karfe 3 na asubahin Asabar, inda suka yi ajalin mutum daya tare da sace biyar.

Ya ce biyo bayan farmakin, ‘yan sanda da mafarauta sun fafata da ‘yan bindigar, lamarin da ya yi sanadin hallak uku lahira daga cikinsu, kwato bindigogin AK-47 guda biyu, harsasai 120, babura hudu, da kuma ceto mutane uku, yayin da rundunar ta ce tana ci gaba da farautar sauran da suka tsere.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata