Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai‘Yan sanda sun kama ɗalibai 11 bisa zargin ajalin wasu abokan karatun...

‘Yan sanda sun kama ɗalibai 11 bisa zargin ajalin wasu abokan karatun su a Kano

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta tabbatar da cafke ɗalibai 11 na makarantar Government Boarding Secondary School, Bichi, bisa zargin hannu a kisan wasu ɗalibai biyu a cikin makarantar.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da hakan a wata saƙo da ya aike wa jaridar Punch a ranar Alhamis.

Ya bayyana cewa an kama ɗaliban ne domin tambayoyi da bincike kan yadda lamarin ya faru da kuma matsayin kowanne daga cikinsu a cikin wannan aika-aika.

Rahotanni sun nuna cewa waɗanda aka kashe, Hamza Idris Tofawa da Umar Yusuf Dungurawa, sun rasu ne sakamakon harin da wasu ɗalibai suka kai musu da wasu ƙarafa da ake kira “Gwale-Gwale”.

A baya, Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dr. Ali Haruna Makoda, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan kisan ɗaliban.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata