Monday, April 6, 2026
HomeLabarai'Yan sanda sun kama mutanen da suka yi wa Sarkin Kano rashin...

‘Yan sanda sun kama mutanen da suka yi wa Sarkin Kano rashin kunya

https://drive.google.com/uc?export=view&id=1odnVNqLO5O-OkoSmTf6StxjAPN2U1IY3
Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta ce ta yi nasarar kama karin wasu mutane uku da ake zargi da kalaman batanci ga Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Bayero.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Usaini Gumel, ne ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Kano.
Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa tun farko rundunar ta kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a lamarin.
Gumel ya bayyana sunayen wadanda ake zargin kamar haka; Abdulrazak Usman Sarki daga Disu Quarters, karamar hukumar Gwale, sai wani mai suna Fatihu Muktar Faruk Kano da kuma Usman Baba Attah, 25, mazaunin unguwar Kabara Quarters, Kano Municipal.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata