Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai'Yan sanda sun kama mutumin da ya sayar da ɗan ‘yar uwarsa...

‘Yan sanda sun kama mutumin da ya sayar da ɗan ‘yar uwarsa jariri kan Naira miliyan 2

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekara 30 bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa ɗan wata guda a kan kudi Naira miliyan biyu.

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya NAN, ya rawaito cewa wanda ake zargin, mazaunin Igbogbo, Ikorodu, ya bayyana cewa ya sayar da jaririn ne domin samun kudin da za a yi jana’izar mahaifiyarsu.

Lamarin ya fito fili ne bayan mahaifiyar jaririn ta kai korafi ga ‘yan sanda.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Olohundare Jimoh, ya umarci a mika binciken shari’ar zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar, wato SCID, da ke Panti, domin zurfafa bincike kan lamarin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata