Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai‘Yan sandan Abuja sun ceto wata mata mai tabin hankali da jaririyarta

‘Yan sandan Abuja sun ceto wata mata mai tabin hankali da jaririyarta

Rundunar ‘yan sandan Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya ta sanar da cewa a ranar 3 ga Afrilu, 2026 da misalin karfe 12:30 na dare, jami’an Rapid Response Squad da ke sintiri a yankin Kwali sun gano wata mata mai tabin hankali da mace a bakin hanya a kauyen Kwaita.

A sanarwar da SP Josephine Adeh ta aike wa DCL Hausa, ta ce jami’ansu sun kai matar da jairiryarta Asibitin Kwali inda aka ba su kulawar lafiya kafin a sallame su cikin koshin lafiya, sannan aka mika su ga jami’in jin kai na karamar hukumar Kwali, Malam Sadiq Kwali.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata