Rundunar ‘yan sandan Uganda ta musanta ikirarin da jam’iyyar adawa ta NUP ta yi cewa an kama jagoranta, Bobi Wine, a daidai lokacin da Shugaba Yoweri Museveni ke gab da sake lashe zaɓen ƙasar da rinjaye.
Jam’iyyar National Unity Platform (NUP) ta Bobi Wine ta ce a daren Juma’a wani jirgin sama mai saukar ungulu na sojoji ya sauka a harabar gidansa da ke Kampala, inda suka “tilasta shi zuwa wani wuri da ba a sani ba.” Sai dai kamfanin dillancin labarai Reuters ya ce bai samu damar tabbatar da wannan ikirari nan take ba.
Kakakin rundunar ‘yan sandan ƙasar, Kituuma Rusoke, ya bayyana a wani taron manema labarai da aka watsa kai tsaye cewa Bobi Wine yana gidansa kuma yana da ‘yancin motsi.
Har lokacin rubuta wannan rahoto, ba a samu jin ta bakin Bobi Wine ko wakilan jam’iyyar NUP ba.
‘Yan sandan Uganda sun ƙaryata kama jagoran adawa yayin da Museveni ke tunkarar sake lashe zaɓe da rinjaye
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
