Tuesday, April 7, 2026
HomeLabarai’Yan ta’adda sun san abin da zai biyo baya duk lokacin da...

’Yan ta’adda sun san abin da zai biyo baya duk lokacin da suka kai hari kan Kiristoci – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa ’yan ta’adda sun san abin da zai same su duk lokacin da suka kai hari kan Kiristoci, yana mai cewa ba za a lamunci irin wadannan hare-hare ba.

Trump ya fadi hakan ne yayin wani jawabi da ya yi, inda ya bayyana matakan da gwamnatinsa ta dauka na kai hari kan kungiyoyin ta’addanci, musamman ISIS, ciki har a Nijeriya da sauran sassan Afirka.

Ya ce a karkashin gwamnatinsa, Amurka ta dauki tsauraran matakai na soja da na tsaro domin raunana ISIS da sauran kungiyoyin ‘yan ta’adda, tare da aikewa da sako karara cewa duk wanda ya kai hari kan fararen hula, musamman wanda ke da alaka da addini, zai fuskanci sakamako mai tsanani.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata