Rundunar ‘yansandan Nijeriya ta bayyana cewa cewa jami’ai sama da 5,000 ne za su yi ritaya a cikin shekarar 2026.
Mataimakin kwamishinan ‘yansanda Sani Doki Yusuf ne ya bayyana haka yayin wani taro da aka shirya wa jami’an da za su yi ritaya cikin 2026 a jihar Kano.
A cewar sa, akwai bukatar dukkanin jami’ai su gaggauta dora bayanan su a shafin yanar gizo na rundunar, domin kaucewa fuskantar kalubale wajen karbar kudaden fansho.
