Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiYunwa ta sa 'yan Nijeriya na neman abinci hannu-baka-hannu-kwarya - Dino Melaye

Yunwa ta sa ‘yan Nijeriya na neman abinci hannu-baka-hannu-kwarya – Dino Melaye

Tsohon dan majalisar dattawa Dino Melaye, ya bayyana cewa matsin tattalin arziki da yunwa a Nijeriya na kara muni, yana mai cewa mutane da dama sun kasa samun abincin da za su ci kullum.

A wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels TV ranar Juma’a, Melaye ya ce halin da ‘yan Najeriya ke ciki karkashin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu bai taɓa faruwa ba a baya.

Melaye, wanda ya wakilci mazabar Kogi ta Yamma, ya bayyana cewa gwamnatin APC ba ta iya jagoranci ba domin har yanzu ta kasa sanya kwanciyar hankali ko nemo mafita ga matsalolin kasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata