Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiYunwar mulki ce ke sa masu hadaka kumfar baki - Gwamna Dikko Radda

Yunwar mulki ce ke sa masu hadaka kumfar baki – Gwamna Dikko Radda

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya soki sabuwar hadakar jam’iyyu da aka kafa kwanan nan, yana mai bayyana wadanda suka kirkiro da ita a matsayin fusatattun da suka rasa mulki.

Dikko Radda ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa a shirin Sunrise Daily na Channels TV a ranar Talata, inda ya ce: “Mu fadi gaskiya. Lokacin ya wuce da za a ci gaba da yaudarar ‘yan Najeriya. Wadanda ke ihu a yau, su suka yi mulki jiya. Mun san tarihin kowa, mun san abin da suka aikata a lokacin da suke cikin gwamnati.”

Sabuwar hadakar jam’iyyu ta amince da jam’iyyar ADC a matsayin dandalin da za su kalubalanci gwamnatin APC ta Shugaba Tinubu.

Gwamnan Katsina ya caccaki hadakar tare da dora ayar tambaya sahihancin manufarta da kuma gaskiyar dalilin kafuwarta.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata