Gwamnatin Jihar Kano ta ce tana sa ran samun haihuwar sabbin jarirai tsakanin 600,000 zuwa 700,000 a shekarar 2026.
Wannan kiyasin ya samo asali ne daga hasashen ƙaruwar yawan jama’a na shekara-shekara da aka yi tun a 2006, wanda ke nuna cewa jihar na da ƙimar ƙaruwa da kashi 3.5 cikin ɗari.
Sakataren hukumar kula da asibitoci na Kano Dr Mansur Mudi Nagoda be ya bayyana hakan a karshen mako, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Sai dai ya yi gargaɗin cewa jihar na fuskantar babban ƙalubale a bangaren lafiya, bayan da yawan mutane ke ƙaruwa fiye da adadin ma’aikatan lafiya da ake da su, inda hakan ke ƙara matsin lamba ga ƙarancin ma’aikata da cibiyoyin lafiya da ake fama da su.
Ya bayyana cewa a halin yanzu jihar na da gibin kwararrun ma’aikatan lafiya akalla 4,000.
