Gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya ce Arewacin Nijeriya na da kwararru da hazikan ‘yan kasa da za su iya magance matsalolin ci-gaba da ake fama da su, muddin manyan yankin suka haɗa kai domin tafiyar hanya ɗaya.
Gwamnan ya bayyana haka ne lokacin da shugabancin Arewa Consultative Forum (ACF), ƙarƙashin jagorancin Alhaji Bashir Dalhatu, ya kai masa ziyara a Kaduna.
Ya ce lokaci ya yi da Arewa za ta tashi tsaye don ta yi aiki wajen warware talauci, gibin ilimi da matsalolin lafiya da suka daɗe suna damun yankin.
Gwamnan ya jaddada cewa Arewa na da dubban kwararru a fannonin kasuwanci, harkokin lafiya, masana’antu, karatu da kirkire-kirkire, waɗanda ake buƙatar haɗa su a wuri ɗaya.
