Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum Umara ya ce, nan da mako daya za a rufe sansanin ‘yan gudun hijira na Muna da ke dauke da ‘yan gudun hijira sama da 11,000.
Sansanin na Muna na daya daga cikin manyan sansanonin ‘yan gudun hijira a jihar wanda aka samar shekaru 10 da suka gabata.
Gwamna Zulum ya bayyana rufe sansanin ne a lokacin da ya kai ziyara a sansanin a makon da ya gabata, inda ya bayyana munanan dabi’un da ake aikatawa a matsayin babban dalilin rufe sansanin.
Ya kuma kara da cewa, dole ne ‘yan gudun hijirar su koma gidajensu domin neman na kansu.
