DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin ministocin da shugaba Bola Tinubu ya nada

-

 

Majalisar Dattawan Nijeriya

Google search engine

A yau ne majalisar dattawa za ta tantance ministocin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika mata domin tantance su.

Daily Trust ta ruwaito cewa hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta yi bincike tare da wanke wadanda aka nada, gabanin tantance su a yau.

A satin da ya gabata ne dai Tinubu ya yi wa majalisar ministocinsa garambawul, inda ya kori ministoci shida tare da nada wasu sabbi bakwai.

Daily Trust ta ruwaito cewa, a ranar litinin wadanda aka nada sun sun je ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin majalisar dattawa, Sanata Basheer Lado, domin gabatar da takardunsu.

Sanata Lado, a wata sanarwa da ya fitar, ya tabbatar da cewa, wadanda aka nada a matsayin ministocin, majalisar dattawa, za ta fara tantance su yau a harabar majalisar a Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara