DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a yi amfani da jiragen soji wajen bai wa masu gyaran lantarkin Arewa kariya-Abdulaziz Abdulaziz

-

 

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu

Google search engine

Tun bayan da Shugaban Tinubu ya nuna fushinsa kan yadda rashin wuta ya addabi yankin Arewa har ya bayar da Umarnin Kan-ta-kwana kan a mayar da wutar, bangarorin da abin ya shafa sun dauki haramar magance matsalar

A wata hira da ya yi da kafar labarai ta DCL Hausa, mai taimaka wa Shugaban Kasa kan harkar yada labarai AbdulAziz AbdulAziz ya bayyana yanda ministan harkokin wutar lantarki ya katse wata ziyarar aiki da yake yi a kasashen waje don amsa kiran shugaban kasa kan ya dawo gida ya dauki aikin gyaran wutar rigi-rigi.

Shi ma Mai bai wa Kasa shawara kan harkar tsaro Malam Nuhu Ribadu tuni ya dukufa, kan umarnin gaugawa da Shugaba Tinubu ya ba shi na samar wa Injiniyoyin gyaran wutan tsaro, inda akan haka ne a yau babban Ministan Tsaron ya biyo sahun sauran wadanda abin ya shafa, wajen bai wa   Shugaban rundunar tsaron Kasa Manjo Janar Kiristofa Musa Umarnin ya gaggauta samar da tsaro ga yankin Shiroro-Kaduna, inda tashoshin da ke bai wa Arewa  harsken lantarki mafi tsoka.

Idan dai ba a manta ba, yankin na Arewa ya shiga duhu na kusan sati biyu sakamakon lalacewar babbar tashar samar da wutar lantarki ga yankin wanda ake zargin ‘yan ta’adda ne suka ragargaza ta. Lamarin da ya janyo durkushewar kasuwanci, kiwon lafiya, da kuma walwalar jama’a a jihohi tara da abin ya shafa

A yanzu da Jami’an tsaro suka fara yi wa yankin kawanya, ana sa ran dawowar wutar kasa da sati daya inji kakakin fadar shugaban kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara