DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An sake fasalta masu magana da yawun Shugaba Tinubu

-

 

Google search engine

Sunday Dare, Daniel Bwala da Bayo Onanuga su ne masu magana da yawun shugaban kasa – fadar gwamnatin Nijeriya. 

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya sake nada mukamai guda biyu na mutanen da za su rika magana da yawun fadar shugaban kasa. 

Wata sanarwa da Hadimin shugaban ƙasa kan yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar, ta ce yanzu ba mutum daya ne zai riƙa magana da yawun shugaban ba. 

Ko baya ga shi Bayo Onanuga, shugaba Tinubu ya amince da naɗa Mista Sunday Dare da kuma Daniel Bwala a matsayin masu ba shi shawara akan yada labarai da harkokin sadarwa. 

Wannan dai wani mataki ne da ake kallo garambawul da gwamnatin ke yi, a cewar jaridar Premium Times.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za a iya kawo karshen matsalolin Arewa aka hada kai – Uba Sani

Gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya ce Arewacin Nijeriya na da kwararru da hazikan ‘yan kasa da za su iya magance matsalolin ci-gaba da ake fama...

Halin kuncin da ‘yan Nijeriya ke ciki ne zai yanke wa Tinubu hukunci a zaben 2027 – NNPP

Jam’iyyun hamayya na NNPP da ADC reshen jihar Osun sun ce halin tsananin talauci da ake ciki yanzu shi ne zai yanke wa shugaban Nijeriya...

Mafi Shahara