DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tarin bashin da kake ciyowa ke jikkata tattalin arzikin Nijeriya, sakon Atiku Abubakar ga Shugaba Tinubu

-

Google search engine

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, ya ce tarin bashin da gwamnatin APC ke ciyowa na kassara tattalin arzikin kasar.

Atiku ya kuma zargi majalisar dokoki ta kasar da zama taimakawa wajen jefa kasar cikin bashi.

Da yake martani kan bashin da majalisar ta amince Tinubu ya ciyo na baya-bayannan, Atiku ya ambato wani rahoto na bankin duniya wanda ya ce ya dora Nijeriya a mataki na uku cikin kasashen da tulin bashi ya yi wa yawa.

Tsohon shugaban ya bayyana damuwa aka yadda gwamnatin ke ci gaba da cin bashi, duk da cewa a watan Yuli shugaba Tinubu ya ce hukumar tattara haraji ta kasa da hukumar kwastam sun samar da kudade ga kasar wadanda ba a taba gani ba.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara