DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tarin bashin da kake ciyowa ke jikkata tattalin arzikin Nijeriya, sakon Atiku Abubakar ga Shugaba Tinubu

-

Google search engine

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, ya ce tarin bashin da gwamnatin APC ke ciyowa na kassara tattalin arzikin kasar.

Atiku ya kuma zargi majalisar dokoki ta kasar da zama taimakawa wajen jefa kasar cikin bashi.

Da yake martani kan bashin da majalisar ta amince Tinubu ya ciyo na baya-bayannan, Atiku ya ambato wani rahoto na bankin duniya wanda ya ce ya dora Nijeriya a mataki na uku cikin kasashen da tulin bashi ya yi wa yawa.

Tsohon shugaban ya bayyana damuwa aka yadda gwamnatin ke ci gaba da cin bashi, duk da cewa a watan Yuli shugaba Tinubu ya ce hukumar tattara haraji ta kasa da hukumar kwastam sun samar da kudade ga kasar wadanda ba a taba gani ba.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar wakilan Nijeriya za ta yi zaman gaggawa kan jadawalin zaben 2027

Majalisar Wakilan Nijeriya za ta koma zama ranar Talata, 17 ga Fabrairu, domin tattauna batutuwan zabe da suka taso bayan sanar da jadawalin zaben 2027...

Kotu ta sahale a binciko takardun karatun Ministan cikin gida na Nijeriya Olubunmi Tunji-Ojo

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta amince da bukatar binciken ingancin takardar shaidar sakandare ta Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo. Mai shari’a Binta Nyako...

Mafi Shahara