DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Malaman jami’ar jihar Kaduna (KASU) sun tsunduma yajin aiki

-

 

Google search engine

Kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, reshen jami’ar Kaduna, KASU, ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani daga ranar 18 ga watan Fabrairu.

Kungiyar ta sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugabanta, Dakta Peter Adamu da sakatarenta, Dokta Peter Waziri, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Nijeriya NAN ya rawaito.

Sanarwar ta ce matakin ya biyo bayan amincewar majalisar zartaswar kungiyar ta kasa. 

Kungiyar ta bayyana daga cikin dalilan shiga yajin aikin da suka haɗa da rashin ingata walwalar ma’aikata da rike musu albashi, wanda ya hada da kashi 60 cikin 100 na albashin watan Satumban 2017 da kuma Mayu zuwa Satumban 2022.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya musanta jita-jitar tsayawarsa takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu har zuwa 2031

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a...

Sau 22 ana yunkurin lalata mana matatar mai – Matatar man fetur ta Dangote

Kamfanin matatar mai ta Dangote ya bayyana cewa tun bayan da matatar man da ke fitar da ganga 650,000 a rana ta fara aiki, aƙalla...

Mafi Shahara