DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Natasha ta maka sanata Nwebonyi a gaban kotu kan zargin bata mata suna

-

 

Natasha Akpoti

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta maka Sanata Onyekachi Nwebonyi a kotu tana neman diyya naira biliyan biyar bisa zargin bata suna da zarge-zargen da ke barazana ga martabarta.

Google search engine

Kotu ta karɓi karar ne bayan Sanata Nwebonyi ya yi wasu kalamai a taron manema labarai da Natasha ke zargin an taba kimarta a zarge- zarge marasa tushe, waɗanda suka shafi mutuncinta da rayuwarta ta siyasa.

Lauyan Sanata Natasha Michael Jonathan Numa, da ya shigar da karar, mai lamba Suit No: W/1359:25 a babbar kotun birnin tarayya Abuja ya ce kalaman sun janyo mata tozarta a idon jama’a kuma suna iya gurgunta aikinta a majalisa.

Sanata Nwebonyi bai mayar da martani ba tukuna, amma ana sa ran kotu za ta fara sauraron shari’ar nan ba da jimawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara